in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi zaben 'yan majalisun dokoki a Equatorial Guinea
2017-11-13 11:13:32 cri
An yi zaben 'yan majalisun dokoki a Jamhuriyar Equatorial Guinea jiya Lahadi, inda kawancen jam'iyyun siyasa guda uku, gami da sauran wasu jam'iyyun siyasar kasar suka shiga takara, domin neman samun kujeru 155 a majalisun dattawa da na wakilai.

Masharhanta na ganin cewa, kawancen jam'iyyun siyasa dake karkashin jagorancin jam'iyyar demokuradiyya ta Equatorial Guinea, za ta ci gaba da samun rinjayen kujeru. Shugaban kasar na yanzu, Obiang Nguema Mbasogo, shi ne mutumin da ya kafa jam'iyyar demokuradiyya, kana shugban jam'iyyar na yanzu. Tun daga shekara ta 1991 har zuwa yanzu, jam'iyyar demokuradiyya ita ce jam'iyya mai mulki a Jamhuriyar Equatorial Guinea.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China