in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Equatorial Guinea ta ce ta murkushe wani yunkurin juyin mulki
2018-01-04 11:10:41 cri
Ma'aikatar harkokin tsaron kasar Equatorial Guinea ta bayar da sanarwa a jiya cewa, gwamnatin kasar ta murkushe wani yunkurin juyin mulki da wasu 'yan jam'iyyar adawa masu tsattsauran ra'ayi suka tsara, kuma wasu sojojin haya asalin kasashen waje suka gudanar.

Sanarwar ta bayyana cewa, a ranar 24 ga watan Disamban bara ma, wasu sojojin haya sun shigo biranen Mongomo, Malabo da Bata na kasar Equatorial Guinea inda suka yi yunkurin kaiwa shugaban kasar Teodoro Obiang Nguema Mbasogo hari a lokacin da ke mahaifarsa ta Mongomo. 'Yan jam'iyyar adawa masu tsattsauran ra'ayi sun yi hayar wadannan sojoji ne, tare da samun goyon bayan wasu kasashen waje.

Sanarwar ta kara da cewa, yanzu haka gwamnatin kasar ta hada kai da hukumomin tsaron kasar Kamru sun kama yawancin mutanen dake da hannu a wannan lamari. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China