in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ofishin watsa labarun majalisar gudanarwar kasar Sin ya bayar da rahoton yanayin hakkin bil adam na Amurka a shekarar 2015
2016-04-14 20:28:20 cri
A yau Alhamis, ofishin watsa labaru na majalisar gudanarwar kasar Sin ya bayar da rahoto game da yanayin hakkin bil adama na kasar Amurka na shekarar 2015, don mayar da martani kan rahoton hakkin bil adama na kasa da kasa da gwamnatin Amurka ta bayar.

A cikin rahoton, an ce ma'aikatar harkokin wajen Amurka ta bayar da rahoton yanayin hakkin bil adama na kasa da kasa na shekarar 2015 a ranar 13 ga wata, inda ta kara nuna ra'ayi ba bisa tushe ba kan yadda hakkin bil adama yake a kasashe daban daban, amma ba ta ce kome ba kan matsaloli masu tsanani da take fuskanta a kan batun.

Rahoton kan yanayin hakkin bil Adama na kasar Amurka na kunshe da kalmomi kimanin dubu 12 da ke shafar batutuwan hakkin jama'a, hakkin tattalin arziki da na al'umma, wariyar launin fata, hakkin mata da kanana yara, da kuma keta hakkin bil adama na sauran kasashe da dai sauransu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China