in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masanin kimiyyar kasa na MDD ya bukaci kasashen Afrika su kara kudaden binciken yanayin kasa
2017-12-06 10:03:24 cri
Wani kwararren masanin kimiyyar kasa na MDD ya bukaci kasashen nahiyar Afrika da su kara adadin kudade a kasafin kudin kasashensu wajen sayen na'urorin bincike game da yanayin kasa wanda zai taimaka wajen samar da abinci a kasashen nasu.

Daniel Pennock, shugaban shirin bada horo kan yanayin kasa a tsakanin gwamnatoci wato (ITPS) karkashin shirin hukumar samar da abinci ta MDD (FAO), ya ce lokaci ya yi da ya kamata a gudanar da binciken domin hakan zai taimaka wajen kiyaye samar da abinci da kare muhalli da kuma lafiyar bil adama sakamakon karuwar da ake samu a tsarin bada kariya ga tsirrai wato (PPP) a takaice. Pennock ya furta hakan ne a lokacin bibiyar rahoton babban taron MDD kan kare muhalli (UNEA) wanda ake gudanarwa a halin yanzu a Nairobi.

Ya ce kasancewa kaso 95 bisa 100 na abinci ana samunsa ne daga kasa, don haka yana da matukar muhimmanci a kula da lafiyar kasa, domin samar da abinci mai lafiya wanda zai inganta lafiyar mutane da dabbobi baki daya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China