in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron karawa juna sani kan ilmin jam'iyyun Sin da Afirka karo na 3 a birnin Beijing
2017-11-29 15:25:22 cri

Yau Laraba ne aka bude taron karawa juna sani kan ilmin jam'iyyun Sin da Afirka karo na 3 a birnin Beijing, ministan harkokin ma'amala da kasashen ketare na kwamitin tsakiyar Jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin Song Tao, da mataimakiyarsa Xu Luping, da kuma wakilai sama da guda 60 na jam'iyyun daban daban daga kasashen Habasha, da Afirka ta Kudu da dai sauran kasashe kimanin guda 20 sun halarci taron.

A jawabin sa yayin bikin bude taron, Song Tao ya bayyana cewa, dunkulewar kasar Sin da kasashen Afirka tana da muhimmanci ga dunkulewar kasa da kasa, kuma bayan da aka yi taron wakilan JKS karo na 18, hadin gwiwar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka ya ci gaba da samun bunkasuwa bisa fannoni daban daban, kuma cikin kyakkyawan yanayi. Kaza lika a matsayin wani muhimmin bangare na tsara manufofin wata kasa, jam'iyyun siyasa sun yi babban tasiri kan bunkasuwar kasa da kasa, da kuma dangantakar diflomasiyya a tsakaninsu.

Ya kuma kara da cewa, bayan shiga sabon zamani, jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ta dukufa wajen yin mu'amala da jam'iyyun kasa da kasa, domin karfafa dunkulewar kasar Sin da kasashen Afirka, da zurfafa fahimtar juna a tsakaninsu a fannin siyasa da kuma karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu yadda ya kamata, ta yadda za a karfafa dunkulewar kasa da kasa baki daya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China