Kasar Sin za ta ci gaba da tsaron jiragen ruwa a mashigin teku na Eden da yankin teku na Somalia
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya furta a yau Jumma'a a birnin Beijing na kasar Sin cewa, kasarsa za ta ci gaba da kokarin halartar ayyuka masu alaka da tsaron jiragen ruwa a mashigin tekun Eden, da kuma yankin teku dake dab da kasar Somalia.
A cewar jami'in, Sin za ta ci gaba da gudanar da aikin ne, don sauke nauyin dake bisa wuyanta na taimakawa sauran kasashen duniya.(Bello Wang)