in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'in gamayyar Larabawa ya nuna kyakkyawar fata ga makomar Lebanon
2017-11-24 09:08:00 cri
Sakatare janar na kungiyar gamayyar kasashen larabawa wato Arab League Ahmed Aboul Gheit, ya bayyana cewa kasar Lebanon zata samu makoma mai kyau a nan gaba, kamar yadda wata sanarwa da ofishin firaiministan kasar Saad Hariri ya fitar.

A cewar sanarwar, Aboul Gheit ya gana da Hariri, kuma ana ganin cewa wannan ganawar tana da babbar ma'ana, kana sun yi shawarwari a tsakaninsu kuma sun amince za su gana a helkwatar kungiyar gamayyar kasashen larabawa a lokacin da Haririn ya ziyarci birnin Cairo na kasar Masar.

A ranar Litinin, Aboul Gheit ya bayyana cewa, Lebanon ba zata taba kasancewa a matsayin wani dandalin yaki tsakanin kasar Iran da kasashen larabawa ba, bayan wata ganawar ta daban da yayi da shugaban kasar Lebanon Michel Aoun da kuma kakakin majalisar dokokin kasar Nabih Berri.

Ministocin harkokin wajen kasashen mambobin kungiyar ta Arab League, sun yi wani taro a farkon wannan mako inda suka yi Allah wadai da Iran da kuma kungiyar Hezbollah, inda suka zargesu da wargaza zaman lafiyar yankin, kuma sun sha alwashin gabatar da wannan batu gaban kwamitin tsaron MDD.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China