in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hariri ya isa Beirut tun bayan da ya yi murabus
2017-11-22 10:40:21 cri
A yammacin jiya Talata ne, firaministan kasar Lebanon Sa'ad Hariri ya isa Beirut, tun bayan da kwatsam ya sanar da yin murabus a wani jawabi da ya gabatar ranar 4 ga watan Nuwamban ta kafar talabijin daga kasar Saudiyya.

Sai dai kuma, shugaba Michel Aoun na Lebanon bai amince da murabus din da Hariri ya yi ba, a ganinsa hakan ya sabawa doka, domin ba a gabatar masa da takardar yin murabus din a kasar Lebanon ba.

Haka kuma, shugaba Aoun yana cewa ,kasar Saudiyya ce ta tilastawa Hariri ya yi murabus, sannan aka yi masa daurin talala, don haka Lebanon take zargin masarautar Saudiya ta neman ta takalar fada.

A jiya ne Hariri ya ziyarci kasar Masar daga birnin Paris, inda ya tattaunawa da shugaba Abdel Fatah Sissi, kana daga bisani ya kai ziyarar ba za ta kasar Cyprus inda nan ma ya tattaunawa da shugaba Nicos Anastasiades.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China