in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na M.D.D. ya bukaci Lebanon da ta gaggauta gudanar da zaben shugaban kasa
2016-03-18 10:44:34 cri
A jiya Alhamis ne kwamintin sulhu na M.D.D. ya fitar da wata sanarwa, inda ya bukaci majalisar dokokin Lebanon da ta gaggauta kada kuri'a don zaben shugaban kasar, ta yadda za a kawo karshen rikicin siyasar kasar.

Sanarwar ta ce, kwamitin sulhu na M.D.D. ya damu matuka game da rikicin siyasar kasar sakamakon rashin shugaban kasa har na tsawon watanni 21. Ya kara da cewa, wannan ya haifar da babban kalubale a fannonin tsaro, tattalin arziki, zamantakewar al'umma da aikin jin kai na kasar.

Don haka kwamitin sulhu na M.D.D. ya bukaci bangarori daban daban na kasar da su hanzarta ganawar majalisar don ganin an shirya zaben shugaban kasar

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, kwamitin sulhu na M.D.D. ya nuna damuwa sosai game da mummunan tasiri da rikicin Syria ya haifar wa kasar Lebanon. Kwamintin sulhu na M.D.D. ya bukaci bangarori daban daban na Lebanon da su guji tsoma baki cikin rikicin da ake samu a kasar Syria.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China