in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tsawwala kiraye kiraye a Jam'iyya mai mulkin Zimbabwe don neman shugaban kasar ya yi murabus
2017-11-18 13:22:27 cri
Kafar yada labarai ta kasar Zimbabwe, ta ruwaito 8 daga cikin kwamitocin larduna 10 na Jam'iyyar ZANU-PF mai mulki, sun yi kira ga shugaban kasar Robert Mugabe ya yi murabus.

Kiran ya zo ne bayan sojoji sun karbe ragamar Gwamnatin kasar a farkon makon nan.

Lardunan, ciki har da mahaifarsa ta Mashonaland ta yamma, na zargin Mugabe da kyale kafuwar wani tsagi cikin jam'iyyar, suna masu kira da a rushe tsagin G40 da suke zargin uwar gidansa Grace Mugabe na jagoranta.

Cikin rahoton da suka fitar, lardunan sun bukaci a mayar da tsohon mataimakin shugaban kasar Emmerson Mnangagwa mukaminsa cikin jam'iyyar da kuma Gwamnati.

Sun kuma ba kwamitin tsakiya na jam'iyyar shawarar gudanar da taro na musammam cikin sa'o'i48 domin sake daidaita jam'iyyar ta yadda za ta dace da yanayin da ake ciki a yanzu.

A nata bangaren, Kungiyar tsoffin 'yan gwagwarmaya da suka yi yakin neman 'yancin kasar, ta yi kira ga al'ummar kasar su yi fitar dango don halartar wani gangami a yau Asabar a birnin Harare, domin mara baya ga matakin da sojojin kasar suka dauka.

Rundunar sojin dai ta ce tana tautaunawa da Mugabe domin daukar mataki na gaba. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China