in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar SADC za ta tattauna batun Zimbabwe a kasar Angola
2017-11-20 11:11:03 cri
Rahotanni daga kasar Afirka ta Kudu na cewa, kungiyar raya kasashen yankin kudancin Afirka wato SADC za ta gudanar da taro a kasar Angola gobe Talata, don tattauna rikicin siyasar dake faruwa a Zimbabwe.

Bayanai na cewa, shugabanni da kusoshin gwamnatocin kasashen Afirka ta Kudu, Angola, Tanzania da Zambia ne za su halarci taron. Yanzu haka shugaban kungiyar SADC na wannan karo, kuma shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma ya tura manzon musamman zuwa kasar Zimbabwe don ganawa da bangarorin da abin ya shafa.

Zuma ya jaddada cewa, kungiyar SADC ba ta goyon bayan duk wani salo na juyin mulkin da ya saba kundin tsarin mulki, ya ce, kungiyar SADC, kungiya ce mai neman zaman lafiya da kwanciyar hankali da kare muradun 'yan kasar, kuma kasar Zimbabwe muhimmin memban kungiyar ce. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China