A rana ta karshe ta ziyarar jami'an diplomasiyya, jami'an da suka hada da jami'in kula da harkokin labarai daga ofishin jakadancin jamhuriyar Nijer da ke kasar Sin Mr. Sidibe Mohamadou Aboubakar, sun kai ziyara garin Xinghua dake lardin, inda suka ziyarci masana'antar sarrafa abinci na Kerisom, da kamfanin sai da kaya ta yanar gizo na Xinghua, tare kuma da wata makarantar midil ta garin. 'Yan makarantar sun kuma kayatar da jami'an da wasannin gargajiya, da wake-wake da raye-raye, don yi musu maraba. (Lubabatu)