A ci gaba da ziyarar da jami'an diplomasiyya ke yi a birnin Taizhou na lardin Jiangsu, a jiya Laraba, jami'an da suka hada da Mr. Sidibe Mohamadou Aboubakar, jami'in kula da harkokin labarai a ofishin jakadancin jamhuriyar Nijer da ke nan kasar Sin, sun kai ziyara gidan tunawa da marigayi Mei Lanfang, wato shahararren dan wasan kwaikwayon gargajiya na Beijing na kasar Sin, wanda dan asalin birnin na Taizhou ne, inda baya ga karin bayani game da rayuwar marigayin, sun kuma kalla tare da gwada fasahar wasan. (Lubabatu)