A jiya Laraba da safe, jami'an diplomasiyya da a halin yanzu suke ziyara a birnin Taizhou na lardin Jiangsu na kasar Sin bisa gayyatar da aka yi musu, sun kai ziyara cibiyar kiwon lafiya da harhada magunguna ta kasar Sin da kuma kamfanin harhada magunguna na Yangtze River da ke birnin na Taizhou. Bayan da aka fadakar da su a kan bunkasuwar harkokin kiwon lafiya da harhada magunguna a kasar Sin, jami'an sun bayyana fatansu na karfafa hadin gwiwa da kasar Sin a wannan fanni. (Lubabatu)