in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNHCR ta bukaci a samo mafita ga matsalar 'yan gudun hijirar Afrika a cikin gida
2017-11-14 09:46:28 cri
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD UNHCR ta ce za ta kaddamar da wani sabon shiri da zai nemi al'ummar Afrika su dauki matakan magance matsalar 'yan gudun hijirah dake kara ta'azzara a nahiyar.

Babban jami'in hukumar ya ce shirin mai suna LuQuLuQu zai mayar da hankali ne kan ilimin falsafar Afrika da ake wa lakabi da Ubuntu ko Ujama, wanda ke da nufin karfafa daukar nauyi tare da raba albarkatu bakin gwargwado da tallafawa juna, wadanda akidu ne dake kunshe cikin al'adu da halayen da 'yan Afirka suka aminta da su.

Hukumar ta ce za a kaddamar da Shirin na LuQuLuQu ne a cikin watan Nuwamba, lokaci guda a kasashe 6 na nahiyar, ciki har da Afrika ta Kudu da Nijeriya da Ghana da Ivory Coast da kuma Senegal.

Kimanin mutane miliyan 20.2 ne ke gudun hijira a Afrika. Akwai kusan rabin miliyan a Kenya, inda kimanin 489,239 daga cikinsu suka kasance mata da yara. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China