in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNHCR ta daura damarar mayar da 'yan gudun hijirar Somalia gida daga Kenya
2017-09-25 11:08:05 cri
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD UNHCR, ta ce ta mayar da 'yan gudun hijira 832 cikin makonni biyu da suka wuce zuwa Somalia, a daidai lokacin da ta daurar damarar kwashe su daga Kenya.

Cikin sanarwar da take fitarwa bayan watanni biyu, hukumar ta ce tsakanin ranar 1 zuwa 15 ga watan nan, an mayar da 'yan gudun hijira 83 zuwa birnin Mogadishu, yayin da aka kai wasu 749 zuwa Kismayo dake kudanci Somalia.

Hukumar ta ce tun bayan kaddamar da aikin a ranar 8 ga watan Disamban 2014, adadin 'yan gudun hijirar Somalia da suka koma gida daga Kenya ya kai 73,031, ciki har da wadanda suka nemi komawa da kansu.

Ta kara da cewa, jimilar mutane 71,034 daga cikin 73,031 ne suka nemi komawa gida da kansu, daga sansanin 'yan gudun hijira na Dadaab dake arewa maso gabashin Kenya.

Gwamnatin kasar Kenya ta ce zaman 'yan gudun hijira na ci gaba da kasancewa barazana ga tsaron kasar da ma yankin baki daya, baya ga matsalar kayakin jin kai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China