Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a karfafa kyakkyawar dangantakar dake tsakanin kasar sa da Vietnam. Shugaba Xi ya bayyana hakan ne, yayin liyafar maraba da mahukuntan Vietnam suka shirya masa.
Ya ce, kasancewar Sin da Vietnam na bin tsarin mulki na kwaminisanci mai salon gurguzu, hadin gwiwar su, da marawa juna baya, tare da neman ci gaba tare, zai dace da biyan bukatun al'ummun su, da wanzuwar zaman lafiya, da daidaito, da ci gaban yankin da suke, da ma sauran sassan duniya baki daya.(Saminu)