in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana goyon kokarin Spaniya na kiyaye dinkuwar kasar
2017-10-30 19:56:45 cri

Yau Litinin ne madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing cewa, batun samun 'yancin yankin Catalonia, harkar cikin gidan kasar Spaniya ce. Kuma kasar Sin ta fahimci kokarin da gwamnatin Spaniya take yi wajen kiyaye dinkuwar kasar, hadin kan al'umma da cikakken yankin kasar. Kasar Sin tana mara wa Spaniya baya a wannan mataki.

A kwanan baya ne, majalisar yankin Catalonia mai cin gashin kai na Spaniya ta zartas da kudurin dokar neman 'yancin kan yankin, tare da yin shelar samun 'yancin kai da neman kafa kasa. Gwamnatin Spaniya ta ce, za ta dauki matakan da suka wajaba kan lamarin, bisa tanade-tanaden da ke cikin kundin tsarin mulkin kasar. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China