in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin hadaka ta Falasdinu ta fara sake fasalin ma'aikatu da sassa a Gaza
2017-10-18 09:50:48 cri

Gwamnatin hadin kan Falasdinu ta fara sauya fasalin ma'aikatu da sassa a zirin Gaza, a wani bangare na yarjejeniyar da aka cimma makon da ya gabata a Masar.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da aka fitar a hukumance, bayan firaministan Falasdinu Rami Hamdallah, ya jagoranci taron majalisar zartarwa na mako-mako a yankin yammacin kogin Jordan.

Sanarwar ta ce, tuni kwamitocin zartarwa na hukumomin gwamnatin da na tsaro da iyakoki suka fara aiki a Gaza.

Ta kara da cewa, gwamnati na da wani cikakken tsari da za ta mika ga dukkan ma'aikatunta dake zirin Gaza, inda ta kara da cewa, daga mako mai zuwa, za a fara gudanar da taron majalisar zartarwar a Gaza da kuma yankin yammacin da kogin Jordan.

A ranar Litinin ne kwamitin gwamnatin Falasdinu ya fara shirye-shiryen mika iyakoki a zirin Gaza, kamar yadda yarjejeniyar ta birnin Alkahira ta tanada. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China