in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: shingen da ake yiwa zirin Gaza na iya sanya matasan yankin son nuna karfin tuwo
2016-10-26 20:36:25 cri
Babban jami'in hukumar MDD mai kula da harkokin bada agaji ga 'yan gudun hijirar falasdinu ko UNRWA a takaice Bo Schack, ya bayyana a jiya Talata cewa, yanayin kafa shinge a zirin Gaza, zai iya sanya matasan yankin fuskantar barazana ta fadawa yanayi na tashin hankali.

A yayin da yake zantawa da manema labaru, Schack ya ce, Isra'ila ta fara kafa shinge a zirin Gaza tun a shekarar 2007, kuma a cikin shekaru uku da suka wuce, an rufe sashen bakin teku dake iyaka tsakanin Gaza da Masar a tsawon lokaci.

Bisa wannan yanayi da ake ciki, masatan yankin za su iya rasa imani game da makomarsu, hakan kuma na iya sanya su kara shiga wasu ayyuka na laifuka, da kara fuskantar barazana ta fadawa yanayin son nuna karfin tuwo. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China