in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala wani kwas din nazarin ci gaban kauyukan kasashen Afirka masu amfani da harshen Faransanci
2017-10-13 09:53:46 cri
A baya bayan nan ne aka kammala wani kwas da aka bude, domin nazarin ci gaban kauyukan kasashen Afrika masu amfani da harshen Faransanci na bana, wanda ma'aikatar cinikayya ta kasar Sin da hadin gwiwar kwalejin kula da harkokin jami'ai na ma'aikatar harkokin noma ta kasar suka kafa.

Jami'ai 47 masu kula da harkokin kauyuka da aikin gona wadanda suka fito daga kasashen Afirka 13, wato Algeria da Benin da Brundi da Kamaru da Kongo Brazaville da Kongo Kinshasa da Cote D'Ivorie da Senegal da Mali da Guinea da Djibouti da Senegal ne suka yi nazarin.

Yayin kwas din, an cudanya ta hanyoyi daban daban da jami'an na kasashen Afirka, kan manufofin raya kauyuka da aikin gona na kasar Sin, da yadda kasar Sin ke kokarin kawar da talauci da yin kwaskwarima kan tsarin kauyuka, da kyautata yanayin halittu a kauyuka da manufar hadin kai tsakanin Sin da kasashen Afirka a fannonin aikin gona da kauyuka da kuma nasarorin da aka samu.

Har ila yau, jami'an sun kai ziyara ga wasu iyalai manoma, inda suka gano yadda ake samun ci gaban aikin gona. Baya ga haka, sun yi bincike a wasu yankunan kasar Sin, don fahimtar yadda ake samun ci gaban kauyuka, inda suka fahimci hakikanin yanayin da wurare daban-aban na kasar Sin ke ciki, wajen raya aikin gona da samun ci gaban kauyuka. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China