Taron dandalin matan Afrika da aka gudanar a karon farko a birnin Marrakech na kasar Morocco, ya samar da wani tsari wanda zai inganta sha'anin shugabanci ga mata.
Bangarori shida ne taron ya cimma matsaya kansu, da suka hada da bangaren aikin gona, makamashi, sana'o'in hannu, bangaren kudi, abinci mai gina jiki, da kuma samar da ruwa.
Yayin taron da aka kaddamar, an bukaci mata 'yan kasuwa na kasashen Afrika su shiga cikin shirin ci gaba wanda aka kebe kudi sama da Euro miliyan 5 don samarwa matan Afrika damammaki, ta yadda za su ciyar da kasashensu gaba.(Ahmad Fagam)