in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rashin kyawawan manufofi game da batun kan iyakoki yana haifarwa kasashen Afrika hasara
2017-09-28 10:05:53 cri

Kwararru sun yi zargin rashin isassun matakan gudanarwa a kan iyakokin kasashen Afrika yana haifarwa kasashen yin hasarar kashi 5 cikin 100 na kudaden shigarsu.

James Kisaale, mataimakin kwamishinan hukumar tattara kudaden shiga na kasar Uganda (URA), ya fada haka a lokacin taron karawa juna sani da aka gudanar a Arusha game da sha'anin kasuwanci, ya bayyana cewa, ana hasarar makudan kudaden shiga a sakamakon rashin isassun manufofin gudanarwa a kan iyakokin wasu kasashen na Afrika, inda aka gano kashi 5 na kudaden shigarsu suna zurarewa.

Jami'in hukumar ta URA, ya buga misali da cewa, kungiyar hada kai da tabbatar da ci gaban tattalin arziki (OECD), ta yi wani nazari a shekarar 2013, inda ta gano cewa, faduwar farashin kayayyaki a duniya zai karu da kashi 1 cikin 100 wanda adadinsa zai zarta dala biliyan 40 na kudaden shiga, yayin da kasashe masu tasowa su ne za su fi cin gajiyarsa.

Kisaale ya bayyana a lokacin taron tattaunawa na wuni guda cewa, bangarorin da za su fi bayar da gudunmowa mafi tsoka a kasashen kudu da hamadar Saharar Afrika sun hada da fannonin fasahar kere kere da saukaka hanyoyin samar da takardun da suka shafi harkokin cinikayya.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China