in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya na shirin yin adabo da kungiyoyin kasa da kasa 90 don rage kudaden da take kashewa
2017-09-28 09:04:19 cri

Gwamnatin Najeriya ta bayyana shirinta na yin ban kwana da kungiyoyin kasa da kasa kimanin 90 wadanda a baya take mu'amala da su, a wani mataki na kara yin tsimin kudi.

Ministan harkokin kudin kasar Kemi Adeosun wadda ta bayyana hakan, ta ce yanzu gwamnati ta kafa wani kwamiti da zai yi nazarin kungiyoyin kasa da kasa da gwamnatin kasar ke mu'amala da su.

A cewar ministar, gwamnatin Najeriya na kashe kimanin dala milyan 70 a kan wadannan kungiyoyi a ko wace shekara, a saboda haka, yanzu Najeriyar za ta ci gaba da hulda da kungiyoyi 220 ne cikin 310. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China