in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da gasar wasan kwallon tebur ta sada zumunta a tsakanin Sin da Zimbabwe
2017-09-21 09:25:30 cri
A kwanakin baya, an gudanar da gasar wasan kwallon tebur ta sada zumunta a tsakanin Sin da Zimbabwe a birnin Harare dake kasar Zimbabwe, inda 'yan wasa daga kungiyar wasan kwallon tebur ta kasar Zimbabwe da kungiyar wasan kwallon tebur ta Sinawa dake kasar Zimbabwe suka shiga gasar. A karshe dai, 'yan wasan kasar Zimbabwe sun cimma zakarar wasan na maza da kuma zakarar wasan na kungiya-kungiya ta maza, kuma 'yan wasa Sinawa sun cimma zakarar wasan na mata da kuma zakarar wasan na kungiya-kungiya ta mata.

Ofishin jakadancin Sin dake kasar Zimbabwe ya dauki bakuncin gudanar da gasar a wannan karo. Jakadan Sin dake kasar Zimbabwe Huang Ping ya bayyana cewa, raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu yana da nasaba da mu'amalar dake tsakanin jama'ar kasashen biyu, ana fatan za a kara fahimtar juna da sada zumunta a tsakanin jama'ar kasashen biyu ta hanyar wasan.

A nasa bangare, ministan wasanni na kasar Zimbabwe Makhosini Hlongwane, ya nuna godiya ga kasar Sin domin ta samar da gudummawa ga kasar Zimbabwe a fannonin wasan kwallon tebur, da iyo, da wasannin motsa jiki. Yana fatan jama'ar kasar Zimbabwe za su ji dadin wasan kwallon tebur kamar Sinawa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China