Bisa labarin da aka samu, an ce, an ji karfin girgizar kasa sosai a birnin Mexico, fadar mulkin kasar, kana an kashe wutar lantarki a wasu yankunan birnin, har an dakatar da tashin jiragen sama a filin jirgin sama na kasar.
Kuma wannan shi ne karo na biyu da aka yi girgizar kasa a kasar ta Mexico cikin makwanni biyu, bayan aukuwar girgizar kasa mai karfin maki 8.2 a yankin gabar ruwa dake kudancin kasar a ranar 7 ga wannan wata. (Maryam)