in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 9 ne suka mutu sakamakon girgizar kasar da ta aukawa kudancin Mexico
2017-09-08 20:03:26 cri

Rahotanni daga Mexico na cewa, mutane a kalla 9 ne suka gamu da ajalinsu lokacin da wata girgizar kasa mai karfin maki 8 bisa ma'aunin Richter ta aukawa yankin gabar ruwan kudancin Mexico a daren jiya Alhamis.

Jami'in sashen kula da tsaron jama'a Jose Garcia ya tabbatar da cewa, mutane 7 ne suka mutu a jihar Chaipas lokacin da gidajen suka rufta, yayin da wasu mutane biyu kuma suka mutu a jihar Tabasco mai makwabtaka.

Ita ma hukumar safiyon kasa ta Amurka ta ce, girgizar kasar ta mamaye kilomita 6 a kudu maso yammacin garin Pijijiapan dake jihar Chiapas, kana ta kai zurfin kilomita 33

Shugaba Enrique Pena Nieto na kasar Mexico ya ce an farfado da tsarin daukin gaggawa na kasa, kana an umarci gwamnatocin kananan hukumomi da su sanya ido tare da gudanar da ayyukan ceto. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China