in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kaddamar da karin taurarin dan Adam na Beidou-3 a bana
2017-09-19 11:05:11 cri

Hukumar kula da tsarin amfani da tauraron dan Adam ta kasar Sin, ta ce kasar za ta kaddamar da karin taurorin dan Adam na Beidou-3 a watan Nuwamban bana.

A cewar shugaban hukumar Ran Chenqgi yayin wani taron fasaha da ya gudana jiya, tsarin amfani da tauraron dan Adam wajen samar da bayanan kasa, zai gudanar da ayyuka ga kasashen dake cikin shirin 'ziri daya da hanya daya a cikin shekarar 2018, sannan zai fadada zuwa fadin duniya a 2020.

A halin yanzu, tsarin na iya samar da hidimomi ga yankuna Asiya da Pasifik.

Sin dai ita ce kasa ta 3 da ta samar da tsarin na amfani da tauraron dan Adam bayan Amurka da Rasha. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China