in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani hadarin kwale-kwale ya halaka sama da mutane 50 a Najeriya
2017-09-15 09:46:56 cri
Rahotanni daga Najeriya na cewa, kimanin mutane 53 ne aka yi imanin sun mutu, lokacin da kwale-kwalen da suke ciki ya yi hadari a kogin Niger dake yankin Bagudo a jihar Kebbi dake arewacin kasar.

Shugaban karamar hukumar Bagudo Muhammade Zagga ya shaidawa maname labarai cewa, hadarin na jiya Alhamis ya faru ne lokacin da kwale-kwalen dauke da sama da fasinjoji 100 ya kife da dukkan mutanen dake cikinsa a tsakiyar ruwa, wadanda aka yi imanin cewa sun halaka. Sai dai har yanzu ana gudanar da aikin ceto ko da za a samu masu sauran numfashi.

Zagga ya kuma tabbatar da cewa, akwai 'yan kasuwa 53 galibinsu daga kauyen Gaya a Jamhuriyar Nijar cikin wadanda wannan hadari ya rutsa da su, a kan sanyarsu ta zuwa cin kasuwa.

Shugaba ya kuma ce hukumomin Jamhuriyar Nijar sun turo gwanayen linkaya don nemo wadanda suka bace.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China