in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta karfafa hadin gwiwa tare da kasashen da suka shiga cikin shirin 'Ziri daya da Hanya daya' a fannin fasahohin sadarwa na zamani
2017-09-15 10:41:39 cri
An gudanar da taron manema labaru dangane da yanayin ci gaban masana'antu da fasahohin sadarwa na zamani a kasashen da suka shiga cikin shirin "Ziri daya da Hanya daya", jiya Alhamis a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Yayin taron, Mista Qu Weizhi, mataimakin shugaban hadaddiyar kungiyar masu sana'ar sadarwa ta zamani ta kasar Sin, ya ce kasar Sin za ta habaka hadin gwiwar dake tsakaninta da kasashen da suka shiga shirin "Ziri daya da Hanya daya" a fannin amfani da yanar gizo ta Internet, da raya fasahohin sadarwa. Haka zalika, za su bude sabon dandali na raya masana'antu, da kafa wani tsari da daidaita ra'ayinsu, don samar da hidima mai inganci.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China