Shugaban Guinea: an zurfafa dangantakar abokantaka tsakanin kasashen Afirka da kasashen BRICS
Shugaban kasar Guinea Alpha Condé ya bayyana a yayin dandalin tattaunawa kan harkokin masana'antu da cinikayya na kungiyar BRICS na shekarar 2017 da aka gudanar a birnin Xiamen na kasar Sin a yau Litinin cewa, ya zuwa yanzu an zurfafa dangantakar abokantaka dake tsakanin kasashen Afirka da kasashen BRICS tare da samun nasarori. Shugaba Conde ya kuma yi kira ga kasashen duniya da su mayar da hankali kan nahiyar Afirka, kana su kulla dangantakar abokantaka a tsakaninsu da kasashen Afirka don moriyar juna. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku