Shugaban Masar: ganawar da aka yi a Xiamen za ta samar da sabuwar damar hadin gwiwa ga kasa da kasa
Shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi ya bayyana a yayin dandalin tattaunawa kan harkokin masana'antu da cinikayya na kungiyar BRICS na shekarar 2017 da aka gudanar a birnin Xiamen na kasar Sin a yau Litinin cewa, taron na birnin Xiamen zai samar da wata sabuwar damar hadin gwiwa ga kasashen duniya, kuma kasar Masar za ta kara yin hadin gwiwa da kasashen BRICS da sauran kasashe masu tasowa a fannonin tattalin arziki da al'adu da sauransu. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku