in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
#BRICS# Shugaban kasar Sin ya bayyana wasu ayyukan dake gaban kasashen BRICS
2017-09-03 16:13:10 cri
Xi Jinping, shugaban kasar Sin, ya yi jawabi a taron dandalin harkar masana'antu da cinikayya na kasashen BRICS na bana dake gudana a birnin Xiamen na kasar Sin, inda ya ce kasashen BRICS na fuskantar muhimman ayyukan da suka kunshi raya tattalin arziki da karfafa hadin gwiwa tsakaninsu.

A cewarsa, za a yi kokarin samun nasarori ta fuskar hadin gwiwar kasashen BRICS cikin shekaru 10 masu zuwa. Don cimma wannan buri, da farko, za a zurfafa hadin gwiwar kasashen don taimakawa kokarin raya tattalin arzikinsu. Na biyu, za a kara daukar nauyin kare zaman lafiya a duniya. Sa'an nan, na uku, za a kyautata tsarin kula da tattalin arzikin duniya. Na hudu kuma shi ne kulla huldar hadin gwiwa da karin wasu kasashe.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China