#BRICS# Xi Jinping: Za a inganta hadin gwiwar kasashen BRICS don kara samun ci gaba a cikin shekaru goma masu zuwa
Da yammacin Yau agogon kasar Sin ne aka bude taron dandalin harkar masana'antu da cinikayya na kasashen BRICS a birnin Xiamen, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabi.
Cikin jawabinsa, Shugaba Xi ya waiwayi tarihin hadin gwiwar kasashen BRICS cikin shekaru 10 da suka gabata, sa'an nan ya yi hasashe kan makomar tsarin BRICS a nan gaba, tare da fatan kasashen, za su inganta hadin kansu cikin shekaru goma masu zuwa.(Kande)