in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mamban musamman mai kula da kare hakkin dan Adam na MDD ya nuna damuwa da kalaman shugaba Trump na zargin kafofin watsa labaru
2017-08-31 11:06:30 cri
Wakilin musamman mai kula da kare hakkin dan Adam na MDD Zeid Ra'ad Al Hussein ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a birnin Geneva a jiya cewa, ya yi bibiyar kalaman da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi game da zargin kafofin watsa labaru da 'yan jarida. Ya yi kashedi cewa, irin wadannan kalaman na iya haifar da matsala ga 'yan jarida.

Zeid ya bayyana cewa, tun bayan da Trump ya hau kan kujerar shugabancin kasar Amurka, yake zargin kafofin watsa labaru har ma a wasu lokutan ya kan kira su da sunan mazambata. Koda a makon da ya gabata yayin da shugaba Trump ya ziyarci jihar Arizona, ya kira 'yan jarida a matsayin marasa gaskiya kana makiyan kasar Amurka. Zeid ya yi kashedi cewa, Trump ya sha zargin kafofin watsa labaru da nuna musu kiyayya, kuma hakan a cewarsa zai haddasa rikici ga 'yan jarida.

Hakazalika, Zeid ya ce, 'yancin watsa labaru yana cikin kundin tsarin mulkin kasar Amurka, kuma wannan shi ne abin da kasar ta Amurka take kokarin tabbatarwa a shekaru da dama da suka gabata. Amma yanzu shugaban kasar yana adawa da wannan manufa, kuma wannan ba abu ne mai kyau ba kuma babban hadari ne ga kasar baki daya. (Zainab Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China