in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
NDLEA ta kama dillalan miyagun kwayoyi guda goma a jihar Adamawa
2017-08-31 09:30:31 cri

Hukumar yaki da masu fatauci da ta'ammali da miyagun kwayoyi a Najeriya (NDLEA) ta ce, jami'anta sun yi nasarar damke wasu da ake zaton dillalan miyagun kwayoyi ne su goma a jihar Adamawa dake yankin arewa maso gabashin kasar.

Kwamandan hukumar ta NDLEA dake jihar Wale Ige ya shaidawa manema labarai a Yole, fadar mulkin jihar Adamawa cewa, an kama wadanda ake zargin ne a cikin makon da ya gabata, biyo bayan sabbin matakan yaki da dillalan miyagun kwayoyi da hukumar ta fara aiwatarwa a fadin jihar, da nufin kakkabe dillalan miyagun dake kokarin bata rayuwar matasan jihar da miyagun kwayoyi.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China