in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Sin za su kara sa ido da tabbatar da 'yancin mallakar yankunan kasar
2017-08-29 09:13:46 cri
Kakakin ma'aikatar tsaron kasar Sin Wu Qian ya bayyana wa 'yan jarida a jiya Litinin cewa, da kimanin karfe 2 da rabi na yammacin wannan rana, bangaren Indiya ya janye dukkan sojoji da na'urorin da ya girke a yankin kasar Sin, kuma bangaren Sin dake wurin ya tabbatar da janyewarsu. Sojojin kasar Sin za su ci gaba da kara sa ido tare da tabbatar da 'yancin mallakar yankunan kasar Sin.

Wu Qian ya bayyana cewa, zaman lafiya a kan yankin dake tsakanin Sin da Indiya shi ne zaman lafiyar yankin baki daya, wanda ya dace da moriyar kasashen biyu da jama'arsu. Sin ta yi kashedi ga kasar Indiya cewa, ya kamata ta koyi darasi daga wannan batun, da martaba yarjejeniyar iyakar kasa da kasa, da ka'idojin dokokin kasa da kasa, da hada kai tare da kasar Sin wajen tabbatar da zaman lafiya a kan iyakar da ke kasashen biyu, da sa kaimi ga bunkasuwar dangantakar dake tsakanin sojojin kasashen biyu. Wu Qian ya kara da cewa, sojojin Sin sun yi imani tare da tabbatar da 'yancin mallakar kasar, da tsaron kasar, da kuma moriyar bunkasuwar kasar, da ba da gudummawa wajen kiyaye zaman lafiya a duniya gaba daya. (Zainab Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China