Ma'aikatar tsaron kasar Sin ta mai da martani kan janyewar sojojin Indiya daga Dong Lang
A yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai dangane da yadda sojojin tsaron iyakar Indiya suka janye daga yankin Dong Lang(Doklam) na kasar Sin a yau Litinin, kakakin ma'aikatar tsaron kasar Sin Wu Qian ya bayyana cewa, sojojin kasar Sin za su ci gaba da kasancewa cikin shirin ko ta kwana, tare da yin iyakacin kokarin kare ikon kasar a shiyyar ta. Baya ga haka, ya kuma gargadi Indiya da ta koyi darasi daga al'amarin da ya gabata.(Lubabatu)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku