in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron kwamitin shari'a na tuntuba na Asiya da Afrika a Kenya
2017-05-04 13:49:15 cri
Daga ranar 1 zuwa 5 ga watan Mayu, aka gudanar da taron kwamitin shari'a na tuntuba na nahiyoyin Asiya da Afrika wato Asian-African Legal Consultative Organization ko kuma AALCO a takaice karo na 56 a birnin Nairobin Kenya.

Shugaban sashin kula da ka'idoji da dokokin shari'a na ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mista Xu Hong ya jagoranci tawagar gwamnatin kasar Sin don halartar taron.

A cikin jawabin da ya gabatar, Xu Hong ya ce, gwamnatin kasar Sin na maida hankali sosai kan raya dokokin shari'a a fadin duniya, da nuna hazaka wajen shiga harkokin kungiyoyin kasa da kasa da na shiyya-shiyya. Haka kuma kasashen Asiya da na Afirka suna taka muhimmiyar rawa wajen kiyayewa gami da raya dokokin shari'a a fadin duniya. Kasar Sin na fatan yin hadin-gwiwa tare da kasashen Asiya da na Afrika, domin tabbatar da adalci yayin da ake amfani da dokokin shari'a a duniya.

An kafa kwamitin shari'a na tuntuba na Asiya da Afrika wato Asian-African Legal Consultative Organization ko kuma AALCO a shekara ta 1956, yanzu tana da kasashe membobi 47 gami da kasashe 'yan kallo guda biyu.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China