Da sanyin safiyar yau Laraba ne wata girgizar kasa mai karfin maki 6.6, ta girgiza gundumar Jinghe a yankin Bortala da ke jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kanta a arewa maso yammacin kasar Sin.
Hukumar dake lura da girgizar kasa ta kasar Sin CENC ta tabbatar da aukuwar bala'in, tana mai cewa, al'ummun birnin Urumqi, da Karamay da Yining dake da nisan kilomita 400 zuwa 200, sun ji tasirin girgizar kasar.
Gundumar Jinghe dai na da yawan al'umma kimanin mutum 140,000.(Saminu)