in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban shirin yaki da matsalar yanayi ya yaba matakan Sin na yaki da matsalar yanayi
2017-08-04 10:46:21 cri
Jagoran kungiyar yaki da matsalar sauyin yanayi na kasar Amurka Ken Berlin ya yabawa matakan da mahukuntan kasar Sin suke dauka game da magance matsalar sauyin yanayi da ke addabar duniya.

Mr Ken Berlin wanda ya yi wannan yabo yayin zantawarsa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a gefen taron kolin hadin gwiwar kasa da kasa, wanda shirin raya kasashe na MDD ya shirya, ya kuma yi gargadin cewa, ficewar Amurka daga yarjejeniyar sauyin yanayi ta Paris, tana iya yin illa ga tattalin arzikin Amurkar.

Jami'in, ya ce kasar Sin tana nuna kyakkyawan shugabanci a duniya, kana tana kan turbar da ta dace a wannan fanni, a hannu guda kuma ya shawarce ta da ta rage dogara a kan makamashin kwal. Ya ce gwamnatin kasar Sin tana daukar managartan matakai a kokarin da take na magance matsalar sauyin yanayi, inda ya ba da misali da shirin shekaru biyar-biyar da mahukuntan kasar suka tsara game da raya makamashin da ake iya sabuntawa. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China