in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan na goyon bayan shirin rage dakarun UNAMID a Dafur
2017-07-20 13:22:54 cri

Kasar Sudan, ta ce a shirye ta ke ta ba da dukkan goyon baya da taimakon da zai kai ga rage jami'an wanzar da zaman lafiya na kawancen MDD da tarayyar Afrika da ke aiki a Darfur (UNAMID), bisa hadin gwiwar gamayyar kwamitoci da aka kafa domin aiwatar da shirin.

Ministan tsaro na Sudan Awad ibn Auf ne ya sanar da haka a jiya, bayan ganawa da karamin sakatare janar na MDD mai lura da ayyukan wanzar da zaman lafiya Jean-Pierre Lacroix, wanda ya kai ziyara kasar domin nazarin yadda za a aiwatar da shawarar MDD ta rage dakarun UNAMID kamar yadda aka tsara. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China