Rahotanni daga Najeriya na cewa, wani sabon fada ya barke tsakanin manoma da Fulani makiyaya a kudancin jihar Kaduna a jiya Talata.
Wata majiyar tsaro ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, sama da mutane 30 ne suka mutu, yayin wasu da dama kuma suka ji raunuka daban-daban a lokacin wannan tashin hankali.
Bayanai na nuna cewa, rikicin ya tashi ne tun a ranar Lahadin da ta gabata, lokacin da matasan Fulkani suka je wani kauye dake Ugwan Uka domin daukar fansa kan kisan da aka yiwa wani shugabansu.(Ibrahim)