in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude bikin baje kolin fina-finan Asiya a Najeriya
2017-07-04 12:07:58 cri

A Jiya Litinin ne, aka bude bikin baje kolin fina-finan Asiya karo na farko a birnin Abuja, fadar mulkin Najeriya. Manufar bikin na kwanaki biyar wanda hukumar kula da harkokin al'adu ta Asiya ta shirya, ita ce yin cudanya tsakanin masana'antar hada fina-finai ta Najeriya mafi girma a nahiyar Afirka da takwarorinta na Asiya.

A jawabinsa yayin bude bikin, jakadan Sin dake Najeriya Zhou Pingjian, ya ce bikin wata kyakkyawar dama ce ta tallata masana'antar hada fina-finan Najeriya, wato Nollywood a nahiyar Asiya.

Jakada Zhou ya shaidawa mahalarta bikin da suka hada da ma'aikatan diflomasiya daga kasashen Asiya da na Najeriya, da masu shirya fina-finai na gida da na ketare, har ma da masu sha'awar kallon fina-finai cewa, dangantakar dake tsakanin Najeriya da Sin da hadin gwiwar Asiya da Najeriya za ta bunkasa har ma a wannan fanni.

Kasashen Asiya kimanin goma ne wadanda suka hada da Sin, Pakistan, Koriya ta kudu, Indonesia, Japan da Thailand da Vietnam, Malaysai da Phillipines da Iran suka halarci bikin.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China