in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi: Sin da Jamus sun shiga wani sabon karni a hadin gwiwar dake tsakaninsu
2017-07-06 10:10:14 cri

Shugaba Xi Jinping na kasar Sin wanda ke ziyara a kasar Jamus, ya bayyana cewa, kasashen Sin da Jamus sun shiga wani sabon karni a dangankatar dake tsakanin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare.

Shugaba Xi ya bayyana hakan ne yayin ganawarsa da takwaransa na kasar Jamus Frank-Walter Steinmeier. Ya ce, a shirye kasar Sin take ta hada kai da Jamus don ganin ta karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu, ta yadda za ta amfani al'ummomin kasashun biyu, su kuma hada kai don tabbatar da zaman lafiya da makoma mai kyau a duniya.

A nasa jawabin, Mr Steinmeier, ya ce, ita ma Jamus a shirye take ta hada kai da kasar Sin don karfafa hadin gwiwar kungiyoyin kasa da kasa kamar kungiyar G20, da ba da gudummawa ga zaman lafiya da ci gaban duniya baki daya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China