in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya yi kira da a gaggauta aiwatar da yarjejeniyar mika mulki a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo
2017-05-05 13:46:24 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya yi kira ga dukkan bangarorin a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo, su gaggauta aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da suka rattabawa hannu a watan Decemban bara, domin mika mulki cikin ruwan sanyi a kasar.

A jiya Alhamis ne mambobin kwamitin sulhun suka bayyana damuwa kan irin kalubalen da aiwatar da yarjejeniyar ranar 31 ga watan Decemban 2016 ke fuskanta, inda suka bayyana cewa, wadanda suka rattaba hannu kan yarjejniyar sun gaza cimma matsaya kan wasu daga cikin tsare-tsaren da wasu daga cikinsu suka rattabawa hannu a ranar 27 ga watan Afrilu.

Sun kuma jaddada kira da a gaggawar aiwatar da yarjejeniya da kyakkyawar niyyar, domin shirya aiwatar da sahihin zabe cikin kwanciya hankali da lumana daga nan zuwa Decemban wannan shekarar, wanda zai kai ga mika mulki kamar yadda kundin tsari da kuma kudurin kwamitin na 2348 ya tanada. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China