in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jama'ar Hong Kong suna gamsuwar ci gaba da yankin ya samu a cikin shekaru 20 da suka wuce
2017-06-30 19:48:42 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yau Jumma'a cewa, bisa goyon bayan gwamnatin kasar Sin, yankin Hong Kong ya samu ci gaba a dukkan fannoni a cikin shekaru 20 da komawar sa bangaren kasar Sin. Jama'ar yankin da m daukacin Sinawa sun gamsu da irin ci gaba da yankin ya samu sakamakon manufar da ake bi a yankin ta kasa daya tsarin mulki iri biyu.

Lu ya bayyana haka ne biyo bayanan kalaman da Boris Johnson, sakataren harkokin wajen kasar Burtaniya ya yi cewa, wai ko yankin Hong Kong zai samu nasara ko a'a a nan gaba wannan na dogaro da iko da 'yanci da hadaddiyar sanarwa ta Sin da Burtaniya ta baiwa yankin. Baya ga haka kakakin ma'aikatar harkokin wajen Amurka shi ma ya bayyana cewa, kasar sa ta damu da yadda ake keta yancin bil-Adama da na watsa labaru a Hong Kong.

Lu ya kara da cewa, kalaman da wasu ke yi, ko yankin Hong Kong ya samu nasara ko a'a a cikin shekaru 20 da dawowarsa bangaren kasar Sin, wannan ba batu ne da ya shafi wasu kasashe ba. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China