in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Zambia ta musanta ba da na goro domin samun tallafi daga IMF
2017-06-28 09:09:44 cri

Gwamnatin kasar Zambia ta musanta zargin da aka yi mata, na baiwa wani jami'in asusun ba da lamuni na IMF na goro, domin ya tallafa mata samun taimako da take nema daga asusun.

Wasu kafofin watsa labarai na yanar gizo dai sun zargi gwamnatin shugaba Edgar Lungu, da baiwa shugaban tawagar IMF Tsidi Tsikata tosiyar baki, yayin ziyarar da ya kai kasar a watan da ya gabata.

Rahotanni sun bayyana cewa, Mr. Tsikata ya gana da shugaba Lungu a yayin ziyarar ta sa, inda suka tattauna game da yiwuwar baiwa kasar ta Zambia damar cin moriyar taimako daga tanajin bashi mai dogon zango da IMF din ke baiwa wasu kasashe.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China