in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kwantar da shugaban Zambia a asibitin Afirka ta Kudu
2015-03-11 09:52:17 cri

Rahotanni daga birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu, na cewa, an kwantar da shugaban kasar Zambia Edgar Lungu a asibitin Milpark dake birnin, domin yi masa tiyasa, biyowa bayan matsalar numfashi da ya fuskanta.

An ce, shugaba Edgar ya yanke jiki ya fadi a ranar Lahadi, yayin da yake jawabin tunawa da ranar mata ta duniya. Bayan an duba lafiyar sa a kasar Zambian ne kuma ya yanke shawarar zuwa Afirka ta Kudu domin samun kulawar kwararru.

Wata sanarwa da ofishinsa ya fitar ta ce, shugaban na fama da matsananciyar gajiya, da kuma alamun zazzabin Maleriya.

Lungu ya lashe zaben shugabancin kasar Zambia a watan Janairun da ya gabata ne bayan rasuwar tsohon shugaban kasar Michael Sata. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China