in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rahoton MDD ya ce adadin 'yan gudun hijira ya yi karuwar da ba a taba gani ba
2017-06-20 10:11:39 cri

Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD, UNHCR ta ce yaki da rikice-rikice da ake fuskanta a fadin duniya na kara raba mutane da muhallansu bisa tilas.

Cikin rahotonta na shekara-shekara kan halin da 'yan gudun hijira ke ciki a duniya, wanda ta fitar jiya a Geneva, hukumar ta ce zuwa karshen 2016 akwai mutane da suka tserewa matsugunansu bisa tilas kimanin miliyan 65.6, kuma 300,000 daga ciki sun kai sama da shekara da tserewa.

A cewar shugaban hukumar Filippo Grandi, babu yadda za a yi a taba amincewa da wannan adadi, yana mai cewa, adadin na kira ne da babbar murya, ga bukatar mara baya ga juna da mai da hankali wajen warware rikice-rikice da kare aukuwarsu.

Daga cikin mutanen miliyan 65.6, miliyan 22.5 'yan gudun hijira ne, adadin da ba a taba gani ba a baya.

A cewar rahoton, rikicin da ake a Syria, shi ne ya fi ko ina a duniya samar da 'yan gudun hijira, inda al'ummar kasar kimanin miliyan 5.5 ke zaune a wajen kasarsu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China